Mahangar Musulunci Kan Asalin Tunani
A yau cikin yardar Allah ga mu dauke da bayani kan mahangar
Musulunci dangane da abin da ya shafi tunani; shin, daga zuci yake samuwa ko
daga kwakwalwa? A mukaddimar da muka
gabatar kan nau'ukan ra'ayoyi dangane da haka, mun fahimci cewa, ta la'akari da
ayoyin Kur'ani da wasu hadisai na Manzon Allah (tsira da aimincin Allah su kara
tabbata a gare shi), tunani na samuwa ne daga zuci, sabanin abin da malaman
kimiyya suke tabbatarwa a yanzu. Amfanin
wannan kasida ta yau shi ne tabbatar da hakan ta hanyar kawo nassoshin Kur'ani
masu Magana kan hakan, da na hadisai.
Domin su ne bayanan da shakku ko kokwanto ba ya shiga cikinsu, saboda
tabbacin da ke tattare da asalinsu. Kuma
tunda mai zancen shi ne ya halicci dan adam wanda muke Magana kan tsarin
halittarsa, ashe kuwa babu wanda zai fahimtar damu gaskiyar abin da ya dangance
shi sai Mahaliccinsa. Bayan haka, za mu
ji mahangar Malaman musulunci kan ma'anonin da suke baiwa wadannan ayoyi ko
hadisai dangane da abin da muke nema na ma'ana a tare dasu.
Kalmar "Zuciya" a Nassin Kur'ani
Daga cikin gabobi ko sassan jikin dan adam, babu bangaren da Allah
ya ambace shi karara, da sunaye daban-daban irin zuciyar dan adam. Wannan a fili yake ga duk makarancin Kur'ani,
masani. Shahararriyar kalma ita ce wacce a asali take nufin Kalmar zuciya
karara, a harshen Larabci. Wannan kalma
ita ce: Al-Qalbu. Allah ya kawo
ta a sigar tilo, watau Al-Qalbu, ya kuma kawo ta a sigar jam'i, watau Al-Quloob. Wannan ita ce Kalmar da tafi shahara
cikin kalmomin da aka yi amfani da su wajen ambaton zuciyar dan adam; musulmi
ne ko kafiri, Annabi ne ko wani gama-garin mutum.
Kalma ta biyu da Allah yayi amfani da ita don nufin zuciya ita ce
kalmar: Al-Fu'aad. Ita ma ta zo a
sigar tilo, watau Al-Fu'aad, sannan ta zo a sigar jam'i, watau Al-Af'idah. Wannan kalma ita ma ta dan shahara a
cikin Kur'ani. Sai kalma ta uku, watau kalmar As-Sadr. Kamar sauran kalmomin da suka gabace ta,
ta zo a sigar tilo da jam'i ita ma.
Watau ko dai ta zo a As-Sadr, ko kuma ka ga tazo da suna As-Sudoor,
watau jam'in Sadr kenan.
Asalin ma'anar Sadr na nufin "kirji" ne a harshen
Larabci. Amma saboda alakar da ke
tsakanin kirji da zuciya, dangane da abin da Allah ke son tabbatar mana don mu
fahimta a aya, shi yasa duk masu tafsiri ke hada alaka tsakaninsa da zuciya,
amma sukan fassara kalmar ne da ma'anarta na asali (watau kirji). Domin kirji
ne farfajiyar zuciya, kuma ganin cewa duk abin da ke cikin farfajiyar nan yana
tasirantuwa da abin da ke ciki, kuma zuciya ce gabar da tafi tasiri cikin
gabobin da ke cikin kirji (tun da a wasu ayoyin an ambace ta karara), sai
malamai su dauka kai tsaye zuciya ake nufi.
Allah shi ne mafi sanin sirrin da ke cikin ma'anonin kalmominsa.
Wadannan kalmomi, a takaice, su ne ke ishara ga zuciya a cikin
Kur'ani. Sannan sun maimaitu a wurare da
dama, wanda hakan ke nuna matukar muhimmancin zuciya ga dan adam wajen fahimta
ko rashin fahimtar sakon shiriya da Allah ya aiko Manzonsa da shi. Kafin mu yi nisa, mu fahimci cewa yawan
ambaton abu, a tsarin zance, na nuna lallai akwai wani muhimmanci – na bayyane
ko na boye – da wannan abin ya mallaka ko yake yi.
Nau'ukan Zukata da Dabi'unsu
Kafin mu yi bayani kan na'ukan zuciya, yana da kyau mu yi bayani
kan dabi'un zuciya. Da farko dai, zuciya
abu ne guda daya, watau dunkulen nama da ke bangaren kirjin dan adam na hagu,
wacce ke aikin famfon jini, kamar yadda bayanai suka gabata. Kuma, kamar yadda Allah ya fada cikin
Kur'ani, bai taba halittar wani dan adam da zuciya guda biyu a kijinsa ba. Wannan sunna ce wacce ya tsara wa kansa, cewa
kowane dan adam zuciya daya ake halittarsa da ita. Daga cikin dabi'un zuci da muka sani a
al'adance, akwai ji irin na tausayi, da so, da kauna. Wadannan su ne manyan
dabi'un da a al'adance muke danganta su ga zuciya. Hatta masana fannin kimiyya da wannan suka
san zuciya, duk da cewa ko a kimiyyance ba za su iya nuna alamar da ke nuna
samuwar soyayya da kauna da suke danganta su gare ta ba (tunda ba abubuwa bane
da ake iya ganinsu); sabanin hujjar da suke da ita kan kwakwalwa.
A daya bangagren kuma, Musulunci ya sanar da mu kari a kan wasu
halayyar da muka sani dangane da zuciya.
Wadannan sun hada da: imani, da kafirci, da munafunci, da tunani, da
fahimta, da rashin fahimta, da karbar gaskiya, da kin gaskiya, da shiriya, da
karkata, da sabo, da niyya, da tsarkakuwa, da baci ko dauda, da karamci, da
fushi, da rashin damuwa, da tsoro, da damuwa, da bakin ciki, da shakka, da
kokwanta, da keta, da tawaye, da nadama, da tabbaci, da rashin tabbaci, da
jiji-da-kai, da kishi, da kuma girman kai.
Wadannan su ne yanayi da dabi'un zuciya, kamar yadda nassoshin Kur'ani
da hadisai ke nunawa. Shi yasa suka kasa
nau'ukan zukata zuwa kashi biyu; da zuciya lafiyayya ko kubutacciya daga kowane
irin cuta, wacce ke dauke da farin ciki, da kwanciyar hankali, da imani, da
gaskiya, da mika lamura zuwa ga Allah, da kuma zuciya mara lafiya, wacce ke
dauke da cututtuka irinsu kafirci, da bidi'a, da shakka kan sakon Allah, da
kokwanto, da girman kai, da zalunci, da yawan sabo, da sauran matsaloli makamantansu.
Wannan rabe-rabe ne da malaman Musulunci suka yi, dangane da bayanan da suka zo
cikin ayoyin Kur'ani da hadisan Manzon Allah (tsira da amincin Allah su kara
tabbata a gare shi) ingantattu.
Dangane da bayanan da suka gabata, idan muka yi dubi sai mu ga cewa
a zahirin lafazi da yanayi, wannan zuciyar da muke dauke da ita a kirjinmu na
bukatar karin bayani kan ayyukan da take yi.
Domin abin da muka sani kawai shi ne, tana aikin rarraba jini ne a jikin
dan adam, wanda hakan ke taimakawa wajen tabbatar da rayuwarsa. Wannan ta sa ra'ayoyin malaman musulunci suka
sha bamban wajen ma'anar kalmar "Al-Qalbu" ko "Al-Fu'aad" a
cikin Kur'ani mai girma. Shin, akwai
wata zuciya ce tattare da asalin zuciyarmu wacce ke gudanar da wadannan ayyuka
amma ba a ganinta, ko kuma ita din ce ke dukkan ayyukan, a bisa kudura da ganin
damar Ubangiji? Ko kuma dai kawai anyi amfani da kalmar ne don nufin wani abu
daban, watau Majaaz kenan?
ABU RAIHAAN, MUHAMMAD IBN AHMAD AL-BAIROONEE
(973 – 1048 MILAD) (2)
Bayan ya
kwashe 'yan shekaru yana wannan aiki ne ya zarce kasar Indiya daga can, lokacin
da Sarki Mahmood ya ci daular Hindu (Indiya) da yaki. Ya kasance tare da shi a
can, kuma a wannan lokaci ne ya rubuta shahararren littafin nan nasa mai suna Kitaabu
Taareekh al-Hind (Littafin Tarihin Hind).
Duk da cewa wannan littafi ne na tarihi kamar yadda sunansa ke nunawa,
amma a cike yake da nau'ukan ilmin kimiyya da fasaha da na sararin
samaniya.
Littattafan
da Ya Rubuta
Abu
Raihaan ya rubuta littattafai masu dimbin yawa. Malaman da suka rubuta
tarihinsa sun yi sabani kan yawan wadannan littattafai na shi. Sai dai adadi mafi karanci da suka bayar shi
ne 146. Daga cikin wannan adadi ko abin
da ya wuce haka, kashi 65 duk a kan ilmin kimiyyar duniya ne (Astronomy), da
fannin lissafi (Mathematics), da fannin lissafi na musamman kan ilmin kasa
(Mathematical Geography), da fannin magunguna (Pharmacology), da fannin
likitanci (Medicine) da dai sauransu. Ya
samu daman rubutu a wadannan fannoni ne musamman saboda baiwar da Allah ya masa
na son ilmi da kuma sanin harsunan duniyar wancan lokaci da yawa da yayi. Domin bayan harshen garinsu mai suna korasmiya,
ya gwanance a harshen Farisanci (Persian), da larabci, da Sanskrit, da
Turkanci, da yaren Girka, da Hibru, da kuma Siriyananci.
Da
wannan ya samu daman kalato ilmin kimiyya da ke makare wajen malaman kasar
Hindu, da Girka, da sauran al'ummomin da yake iya magana da harshensu. Bai tsaya wajen kalatowa kadai ba, ya yi geji
a tsakaninsu, inda ya watsar da na watsarwa; musamman wadanda suka saba wa ka'idar
musulunci. Misali, ya fafata da Shehin
malamin nan mai suna Ibn Sina, kan abin da ya shafi dogaro da kuma yarda da
ka'idojin malaman Falsafar daular Girka, wadanda Ibn Sina ke bi sau da
kafa. Ba komai ya kawo haka ba sai don galibin
sakamakon bincikensu na kimiyya a cakude yake da akidunsu na maguzanci.
Har
zuwa yau duniyar kimiyyar sararin samaniya na tinkaho da Abu Raihaan. Domin ta dalilin bayanan da ya tara kan
yanayin Wata da alakarsa da Rana a lokacin da dayansu yake husufi ne, a yau aka
gano tsarin gudanuwar Wata wajen tafiya (watau Moon Acceleration), abin
da Dunthorne ya tabbatar a shekarar 1749.
Bayan haka, har zuwa yau ana amfani da bayanansa kan binciken da ya
gudanar dangane da halittun da ke sararin samaniya – Rana, da Wata, da Taurari
da yanayin gudanuwarsu. Har wa yau Abu
Raihaan babban malami ne kan abin da ya shafi ilmin zanen taswira, watau Cartography. Domin yana cikin wadanda ake dogaro da
zanensu kan Tsohuwar Taswirar Duniya (watau Old Global Map).
Daga
cikin manyan littattafansa akwai babban littafinsa kan tsarin tunani da al'adun
mutanen daular Hindu mai suna Tahqeequ Maa Lil Hind Min Muqawwilatin Fil
'Aqli, Ma'aqoolatan am Marzoolatan, wanda a harshen Turanci ake kira Indica. Littafi ne da ke bayanin dabi'u da al'adu
da kuma addinan mutanen kasar Indiya.
Sai kuma wani littafi mai suna Kitaabut tafheem Li-awaa'il Sinaa'atit
tanjeem, wanda a harshen Turanci ake kira The Book of Instruction in the
Elements of the Art of Astrology. Littafi
ne da ke bayanin hakikanin ilmin taurari. A cikin littafin ne Abu Raihaan ya
bambance tsakanin ilimi kan taurari da rayuwarsu, da yanayinsu, da tasirinsu a
sararin samaniya, duk a kimiyyance, da kuma ilimin taurari da bokaye ke amfani
da shi wajen ikirarin sanin gaibu, ko wani mummunan lamari da ake tunanin zai
faru idan tauraruwa kaza ta bullo a misali.
Nau'in ilimin taurari na farko, a cewarsa, shi ne abin da ya kamata a
koya kuma a karantar da al'umma, saboda alakarsa da addini kai tsaye. Amma nau'in ilimin taurari na biyu, shedanci
ne, kuma musulunci bai yarda da shi ba. Domin taurari halittun Allah ne kamar
sauran halittu, ba su da wani tasiri na musamman a bisa karankansu dangane da
canza rayuwar mutane wajen samu ko rashi, wajen amfani da ko cutarwa.
Littafi
na gaba shi ne Al-aathaarul Baaqiyah, anil Quroonil Khaaliyah, littafin
da ke bayani kan tarihin al'ummomin da suka gabata, da irin tasirin da suka yi
cikin abin da suka bari na kimiyya a duniya.
A cikin littafin yana kokarin gwama tsakanin al'ummomin da suka gabata
ne, da irin tasirin da suka yi wajen barin wani abu da ake dogaro da shi na
kimiyya. Kamar irin fasaharsu wajen gano
shigan wata, da karewarsa, da amfani da taurari wajen gano bigiren wasu garuwa
ko kasashe. A takaice dai littafi ne na
tarihi, wanda ke cakude da ilimin sararin samaniya, da lissafi, da kuma tarihin
al'ummomin da suka shige. Sai kuma
littafi mai suna: Qaanoonul Mas'oodi.
Littafi ne na kamus kan abin da ya shafi kalmomi na musamman, da
fannoni na musamman, da malamai shahararru kan ilimin Sararin samaniya, da
lissafi, da ilimin kasa, da fasahar gine-gine.
Ya sadaukar da littafin ne ga daya daga cikin 'ya'yan Sarki Mahmood
Al-Ghaznawi, mai suna Mas'ood. Turawa
kan kira littafin da suna: The Mas'udi Canon.
Sai
littafi na gaba mai suna: At-tafheem Li Sinaa'tit Tanjeem. Littafi ne mai dauke da tambayoyi da amsa
kan ilimin taurari da bambance-bambancen da ke tsakanin nau'ukan ilimin taurari
kamar yadda bayani ya gabata a baya, da ilimin lissafi, da ilimin sararin
samaniya. Ya rubuta shi da Larabci,
sannan ya juya shi zuwa harshen Farisanci. Sai littafi da ya rubuta kan
sinadaran da ke karkashin kasa wadanda Allah ya tanada wa bayinsa mai suna: Al-Jamaahir
fee Ma'arifatil Jawaahir. A harshen
Turanci ana kiransa Gems. Ya
sadaukar da wannan littafi ne ga daya daga cikin 'ya'yan Mas'ud mai suna
Mawdood. Sai kuma littattafan da ya rubuta na tarihin garin Khawaarizm,
da tarihin Mahmud Al-Ghaznawi da mahaifinsa, da kuma fasahar gano bigire a
duniya mai suna Astrolobe da ya
kera, sai littattafan da ya rubuta kan ilimin magunguna da harkar likitanci.
Dukkan
wannan kokari da yayi suna nuna tsananin kwazonsa ne wajen tabbatar da ilimi,
da son ciyar da al'umma gaba, da kuma karfin imani da sakamakon da Allah ya
tanada wa masu ayyuka kyawawa. Kamar
sauran mutane masu numfashi, Abu Raihaan bai dawwama ba a duniya shi ma. A
karshe Allah ya karbi rayuwarsa. Bari in
barku da daya daga cikin manyan abokan karatunsa mai suna Abul Hasan 'Ali bn
'Eesa, wanda ya zanta da shi cikin numfashinsa na karshe. Ga abin da yake cewa:
“Na ziyarci Abu Raihaan
a lokacin da yake fama da cutar ajali.
Ina shiga inda yake, nan take na gane cewa lallai ya kusa barin wannan
duniya. A cikin wannan hali ne yake
sanar da ni cewa, a haduwarmu ta karshe lokacin da muke tattaunawa kan wata
mas’ala da ta shafi rabon gado, akwai wani abu da na fada, wanda daga baya ya
gane cewa kuskure ne. Nan take sai na
tausaya masa, har na ke ce masa ai yanzu ba lokacin da ya kamata a tattauna
batu irin wannan bane; musamman ganin halin da yake ciki na rashin lafiya. Sai ya ce mini, “Ai ni tuni na san zan bar
wannan duniya, amma kuma ba ka ganin ya dace a ce in fahimci wannan mas’alar,
da a ce na mutu da jahilcinta?” Daga nan
sai na maimaito masa abin da na fada, sannan ya fara mini bayani
dalla-dalla. Muna gama wannan tattaunawa
da shi, sai na tashi na fita. Fita na ke
da wuya, sai na fara jin kururuwa, daga nan na fahimci cewa lallai ya
rasu. Rayuka masu daraja irin wadannan
ne ke kasancewa cikin karfi da kuzari har zuwa numfashinsu na karshe.”
Abu Raihaan
al-Bairooni ya rasu ne ranar 13 ga watan Disamba ta shekarar 1048 miladiyya,
daidai da shekara ta 387 kenan bayan Hijira, yana dan shekaru 75. Allah gafarta masa, ya kuma sanya Aljanna
makomarsa da mu baki daya.
No comments:
Post a Comment