Sabanin Ra'ayi kan Ma'anar
Zuciya a Larabci
Kamar sauran ayoyin da suka
zo kan wasu mas'alolin shari'a, Malaman tafsiri sun sha bamban wajen fahimtar
ma'anar kalmomin da ke nuni zuwa ga zuciya a Kur'ani da Hadisai ingantattu. Wasu sun dauki kalmar a zahirin ma'anarta
kamar yadda Allah ya kawo ta, basu mata tawili ba. Ma'ana, basu karkatar da ma'anarta zuwa ga
wani abu daban ba. Wasu kuma sun dauki
kalmar zuciya ("Al-Qalbu", ko "Al-Fu'aad", ko kuma
"As-Sadr") a matsayin Majaaz ne. Watau kalmar da ke wakiltar wani abu daban,
amma ba ita ake nufi ba. Suka ce abin da
ake nufi shi ne "Hankali" ko kuma "Basira."
Bayan haka, wadanda basu yi
wa wadannan ayoyi ko kalmomi tawili ba wajen tafsiri, suna dogaro ne da cewa,
daga cikin ayoyin da Allah ya ambaci zuciya, akwai inda ya ambace ta yana mai
danganta ta ga tunani ko hankaltar abubuwa.
Har wa yau, akwai kuma ayoyin da Allah ya ambaci kalmar zuciya tare da
mahallin da take, watau kirji kenan. In kuwa haka ne, a cewar masu wannan
ra'ayi, lallai akwai alakar da ke nuna
dangantaka a tsakaninsu, dangantaka mai karfi kuwa. Domin Allah ba zai ayyana abu, tare da
muhallinsa, ya kuma danganta masa wani aiki na musamman ba, face akwai hakan
tare da abin da Allah ya ambata. Domin
daga cikin sifofin Allah madaukakin sarki shi ne, Mai hikima ne shi, yana dora
kowane abu ne a mahallinsa; ba ya yin wani zance wacce ba ta bayar da fa'ida.
Suka ce wuri na farko da
Allah ya ambaci zuciya yana alakanta ta da tunani shi ne cikin Suratul A'araaf,
aya ta 179, inda yake cewa: "Kuma
lalle ne hakika, mun halitta, saboda Jahannama, masu yawa daga cikin aljannu da
mutane; suna da zukata, ba su fahimta da su…." Suka ce Allah ya ambaci zukata (na mutane
da aljannu), sannan yace ba su fahimta da su.
Fahimta kuwa, a cewarsu, ba ta samuwa sai ta hanyar tunani. Wuri na biyu na cikin Suratul Taubah aya ta
87, inda Allah ke cewa: "…Sun yarda
da su kasance tare da mata masu zama (a cikin gidaje). Kuma aka rufe a kan
zukatansu, saboda haka, su, ba su fahimta." A nan Allah na ishara ga munafukan madina
da suke kin zuwa yaki, da sakamakon da ya biyo bayan wannan mummunar akida
tasu, ga zuciyarsu. Ma'anar da wannan
aya ke bayarwa iri daya ne da wanda ta gabace ta. Sai wuri na uku cikin Suratun Nahali aya ta
108, inda Allah ke cewa: "…wadancan
ne wadanda Allah ya bice hasken zukatansu da jinsu da gannansu. Kuma wadancan
su ne gafalallu." Suka ce
wannan aya ma tana nuna cewa lallai zukata na yin tunani. Domin idan babu
tunani, babu yadda za a yi gafala, ko shagala da wani abu mai muhimmanci, ya
samu. Sai wuri na hudu cikin Suratul
Israa'i aya ta 36, inda Allah ke cewa: "Kuma
kada ka bi abin da ba ka da ilimi game da shi.
Lalle ne ji da gani da zuciya, dukkan wadancan, (mutum) ya kasance daga
gare shi wanda ake tambaya." Suka
ce wannan ke nuna cewa lallai zuciya na tunani.
Domin an hana mutum yanke hukunci ne da jahilci. Idan kuwa zuciya ta zama babu ilimi a
cikinta, to, za a rasa yakini (watau karfin tabbaci da irada) a tare da
ita. Idan aka rasa yakini a cikinta, to
babu abin da zai maye gurbin ilimi sai jahilci.
Shi kuma jahilci alamunsa su ne shakku da rashin tabbas, da dimuwa. Su kuma wadannan dabi'u ko yanayin zuci suna
samuwa ne ta hanyar tunani. Idan babu
tunani, babu yadda za a yi a samu shakka ko dimuwa irin ta zuci.
Sai wuri na biyar, cikin
Suratul Kahfi aya ta 28, inda Allah ke cewa: "…kuma kada ka bi wanda muka shagaltar da zuciyarsa daga
hukuncinmu, kuma ya bi son zuciyarsa…"
Mun yi bayani a baya cewa babu yadda za a yi a samu shagala ba tare
da tunani ba. Sai wuri na shida cikin
Suratul Hajji aya ta 46, inda Allah ke cewa: "Shin, to, basu yi tafiya ba a cikin kasa, domin ya zama suna da
zukata wadanda za su yi hankali da su, da kunnuwa da za su saurare da su a tare
da su? Domin lalle ne idanun ba su
makanta, amma zukata wadanda ke a cikin kiraza su ke makanta." Suka ce wannan aya na nuna abu biyu. Na farko Allah ya kalubalanci kafirai da suyi
tafiya a cikin kasa su ga yadda ya hallakar da wasu al'ummomin da suka gabace
su, wannan zai sa su hankalta da zukatansu. Hankalta da abu kuma, kamar yadda
muka sani, ba zai yiwu ba sai ta hanyar tunani.
Ba wai su kalli abin su san yana nan ake nufi ba, ba irin wannan
hankaltar ake nufi ba. Ana nufin su dauki darasi, su kokkoma da zukatansu
kan abin da suka gani. Wannan kuwa
shi ake kira tunani. Abu na biyu shi ne
makantar zuci, wadda ke cikin kiraza. Ma'ana zuciyar da muka sani din nan dai,
ita Allah ke nufi, a cewarsu. Sai wuri
na bakwai da ke cikin Suratu Muhammad, aya ta 24, inda Allah ke cewa: "Shin to, ba za su yi tunani bane kan
Kur'ani, ko kuwa a kan zukatansu akwai makullansu ne?" Wannan aya tana magana ne kan tunani
dangane da ayoyin Kur'ani, da gaskiyar zantukan da ke cikinsa. Allah ya ce ko akwai makullai ne da suka
kulle zukatan kafirai, da har suka kasa yin tunani kan Kur'ani? A nan Allah ya ambaci rashin tunani, ya
alakanta shi da kullewar zuciya. Wannan
ke nuna da zuciyar a bude take, da tunani ya samu.
Sai wuri na karshe cikin
Suratun Naas aya ta 5, inda Allah ke cewa: "…wanda
ke sanya wasuwasi a cikin kirazan mutane."
Wannan aya tana magana ne kan tasiri da gamewar wasuwasin shedan ga
zuciyar dan adam. Sai aka ambaci
mahallin da zuciyar take, watau kirji kenan, don nuna cewa lallai wasuwasin
shedan na da gamewa da kuma tasiri mai karfi wajen sabo. Shi
wasuwasi wani irin zancen zuci ne mai dauke da umarnin aikata sabo, wanda bawa
ke ji a tare da shi. Duk sadda ka ji
kana son ka aikata wani aikin sabo, to ka san cewa lallai wannan jin da kake ji
a zuciyarka, wasuwasi ne na shedan.
Wannan, a cewarsu, alama ce da ke nunawa a fili karara, lallai zuciya na
tunani. Domin da ba ta tunani babu yadda
za a yi dan adam ya bijire wa dukkan wasuwasin shedan, wanda kuma a halin yanzu
ba haka lamarin yake ba. Ma'ana ba
dukkan wasuwasin shedan bane yake tasiri wajen sa dan adam ya aikata sabo, in
kuwa haka ne, kenan ashe zuciyar dan adam na tunani, wajen tantance irin
umarnin da take samu a cikinta, kafin ta baiwa gabobin jiki umarnin
aikatawa. Bayan haka, akwai hadisin
Nu'umanu dan Bashir wanda a karshensa Manzon Allah ke cewa: "…kuma lallai a cikin jiki akwai wani
gudan tsoka; idan ya gyaru, jiki gaba dayansa ya gyaru. Kuma idan ya baci, to, jiki gaba dayansa ya
baci. Ku saurara, ita ce zuciya." Dukkan wadannan nassoshi na ishara ne
zuwa ga wannan zuciyar da ke cikin kirjinmu, kamar yadda yazo karara a cikin
wannan hadisi.
Tantance
Hakikanin Lamarin
Daga bayanan da suka gabata,
za mu fahimci cewa lallai akwai wani lamari tattare da wannan bangaren jiki da
ake kira zuciya; shin, da ra'ayin masu cewa "hankali" ake nufi da
kalmar "Al-Qalbu", ko na masu cewa hakikanin "Zuciyar" ake
nufi. Domin a cikin Kur'ani an danganta
"hankali" ga zuciya. An
danganta "tunani" ga zuciya.
An danganta "rai" ko "ruhi" ga zuciya. An danganta "An-Nafs" (watau
"zati" ko "hakikanin mutum") ga zuciya. An kuma danganta "fahimta" ga
zuciya. Dukkan wadannan kalmomi an kawo
su a wurare daban-daban, a sigogi daban-daban, inda kalmar "Al-Qalbu"
ke wakiltarsu, kamar yadda wasu malamai suka fassara. Amma abin da aka fi danganta shi ga zuciya
shi ne "hankali". To, ko ma
dai mene ne, akwai wani sha'ani da ke
tare da wannan zuciya da Allah ya halitta mana.
Domin yawan Ambato – a Kur'ani, da Hadisi, da zantukan Malamai, da
littattafansu, da kasidunsu – duk yana tabbatar da haka.
Wannan ishara da nassoshin
shari'a suka yi ga zuciya ya sa manyan Malaman musulunci gaba daya sun mayar da
hankulansu zuwa ga wannan bangare na jiki.
Suna masu danganta ayyuka daban-daban gare ta, wadanda suka shafi
halayya da dabi'unta – irinsu imani, da taqawa, da yarda, da kunya, da kara, da
tawakkali, da sauransu. Kari a kan haka,
sukan hada da "tunani", daga cikin ayyukan da suka shafi zuciya. Wannan a fili yake cikin rubuce-rubucensu.
Abdullahi bn Mubaarak, daya daga cikin manyan magabata ya rubuta littafi mai
suna: "Az-Zuhd", mai dauke
da bayanai kan dabi'un zuci da za su taimaka wa musulumi rage burinsa a rayuwa,
don fusktanr lahira. Imamul Ghazaali,
Abu Haamid, shi ma ya yi bayani mai tsawo a shahararren littafinsa mai suna: "Ihyaa'u Uloomad Deen", da
wani littafi dan karami mai suna: "Mukaashafatul
Quloob" inda a ciki ya ware babi na musamman kan tunani, wanda hakan
ke nuna cewa lallai tunani na daya daga cikin ayyukan zuciya. Bayan Ghazaali
sai Abul Qaasim Al-Qushairee, a cikin shahararren littafinsa mai suna: "Ar-Risaalatul
Qushairiyyah." Wanann littafi
na dauke ne da bayanai kan ayyukan zuciya, wadanda mutum zai lazimce su don
gina kyakkyawar alaka tsakaninsa da Allah.
Bayan shi sai Al-Imam Ibn Al-Qayyim, daya daga cikin manyan malaman
kasar Sham a karni na 7. Ya yi bayani
mai tsawo a cikin littafinsa mai suna: "Maddarijus Saalikeen, Baina Manaazili
Iyyaaka Na'abudu wa Iyyaaka Nasta'een," wanda sharhi ne na littafin
Imamul Harwee kan dabi'un zuci, masu karfafa imani da alaka tsakanin bawa da
Ubangijinsa. A cikin littafin ya ware
babi na musamman kan tunani, ya kuma alakanta hakan ga zuciyar bawa, don samun
kyakkyawar saitin imani.
Daga cikin malaman wannan
zamani akwai Sheikh Muhammad bn Saalih Al-Munajjid, ya rubuta littafi mai suna:
"A'amaalul Quloob," watau
"Ayyukan Zukata." A ciki ya
ware babi musamman kan tunani, ya kuma kawo wasu daga cikin ayoyin da muka yi
bayani kansu a baya. Daga shi sai Dakta
Khaalid bn Abdulkareem Al-Laahim, farfesa mai karantar da fannin karatun Kur'ani
a Jami'ar Muhammad bn Sa'ood na kasar Saudiyyah. Ya rubuta littafi mai suna: "Qiraa'atun Bi Qalbin," ma'ana:
"Tsarin Karatu da Zuciya." A
shafi na 5, ya kasa nau'ukan karatu, ta la'akari da wajen yinsu, zuwa kashi
uku. Kashin farko shi ne yin karatu a bayyane, wanda ya kunshi motsa labba da
harshe, da fitar da sautin da ake ji.
Sai kashi na biyu da ya kunshi yin karatu a asirce, ta hanyar motsa
labba da harshe, amma mai karatu kadai ke jiyar da kansa. Sai kashi na uku
wanda ya shafi yin karatu cikin sirri ba tare da motsa labba da harshe ba, sai
dai zuciya kadai. Ya kuma kasa nau'in
karatu da zuci zuwa kashi uku; na farko yin karatu a asirce ta hanyar amfani da
idanu da kuma zuciya. Na biyu ta hanyar amfani da zuciya da tsantsar hadda da
aka yi a baya. Na uku kuma yin amfani da zuci kadai. Wannan, a cewarsa, tsantsar tunani ne. A shafi na 6, ya kasa nau'ukan zancen zuci
zuwa kashi uku. Na farko shi ne yin magana da zuci kadai, wannan tunani
kenan. Na biyu shi ne yin zance da zuci
da kuma harshe; ya zama zancen zuci ne harshe ke furutawa. Sai na uku, watau yin zancen zuci da harshe,
amma ya zama zancen harshe ya saba wa abin da zuciya ke furutawa (ko tunani ko
tattaunawa a kai) – wannan, a cewarsa, shi ne munafunci, wanda da shi ne Allah
ya sifata munafukai kan abin da ya shafi imani.
Abubuwan
Da Ke Dabaibaye da Zuciya
Daga bayanan da suka gabata
za mu fahimci lallai zuciya, wato wannan gudan tsoka da ke kirjinmu, tana da
bubuwa da yawa da suka dabaibayeta, masu sa a ambace ta maimakon a ambace su. Wannan ba ya nuna cewa ita kanta ba ta da
wani tasiri, a a, akwai alamun ita ma tana da nata tasirin. Ababen da suka dabaibaye zuciya su ne:
"Hankali" (Mind/Sense of reasoning), da "Ruhi" ko
"Rai" (Soul), da "An-Nafsu," watau "zati" ko
"hakikanin dan adam" (Self), da "Fahimta"
(Understanding/Comprehension), da kuma "Al-Hayaatu", watau
"Rayuwa" (Life). Malaman Musulunci masana harshen Larabci da ilimin
shari'a sun nuna cewa, "Ruhin" dan adam (Human Soul), idan tana cikin
jikinsa, ita ce ke wakiltar "zatinsa" ("An-Nafs"), wannan
ke sa ya samu "Rayuwa" (Life), har ya zama mai hankali, mai tunani –
iya gwargwadon shekarunsa. Da
"Fahimta", da "Irada", da "Ilimi", duk suna
rataye ne a jikin hankalin dan adam.
Daga cikin wadanda suka yi wannan namijin kokari akwai Taajul Lugha,
Muhammad ibn Qaasim, wanda aka fi sani da "Al-Ambaari", cikin
littafinsa mai suna: "Al-Adhdhaadu
Fil-Lugha," da kuma babban Malamin Lugha, watau
"Al-Jarjaanee", cikin littafinsa mai suna: "At-Ta'areefaat."
To shi kuma hankali, wanda ke
rataye da ruhin dan adam mai dauke da wadancan al'amura masu ban al'ajabi, a
ina yake damfare a jikin dan adam? Daga
cikin wadanda suka amsa wannan tambaya akwai Dakta Kareema Mutawalli
At-Tookhee, cikin littafinta mai suna: "Quloobun
Ya'aqiloona Biha," shafi na 7, bayan ta kawo ayar da ke Suratul Hajj
(aya ta 46), ta bibiye ta da sharhin malaman tafsir, a karshe tace: "Wasu
masana suna cewa 'Mahallin hankali shi ne kwakwalwa da ke kai', hujjarsu ita
ce, a duk sadda aka daki mutum a ka duka mai karfi, yakan rasa hankalinsa. Amma ingantaccen zance shi ne, zuciya ce ke
dauke da hankali, kamar yadda bayanai suka gabata." Wannan shi ne ra'ayin Shawkaani, da Qurtubi,
da As-Sa'aalabee da kuma Sheikhul Islam Ibn Taimiyyah; manyan malaman tafisirin
Kur'ani. Shi ne kuma ra'ayin Abdullahi
dan Abbass (Allah kara masa yarda).
Mako mai zuwa in Allah ya
kaimu, za mu kawo bayanai kan sabon nau'in binciken kimiyya da ake kan yi
dangane da alakar da ke tsakanin zuciya da kwakwalwa, bayan nan ne za mu sani,
a ilimance, wani bangare ne daga cikinsu ke samar da tunani.
No comments:
Post a Comment